1

1 Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
2 Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;
3 Mai rahama, Mai jin ƙai;
4 Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.
5 Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.
6 Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.
7 Hanyar waɗanda Ka yi wa ni´ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.