99

1 Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
2 Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
3 Kuma mutum ya ce "Mħ neya same ta?"
4 A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
5 cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
6 A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
7 To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
8 Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.